<![CDATA[Hatsarin Noma A Inda Babu Tsaro | RSS.com]]>

Saurara a: Apple Podcast | Spotify | RSS


Da can kana shafe tsawon kwanaki a gona, kana shuka iri-iri na amfanin gona kana dawowa gida da girbi mai yawa. Yanzu kuma, sa’o’i kaɗan kacal kake aiki, a ƙarƙashin sa ido na sojoji. Ba za ka iya yin nesa da gari ba, kuma ba za ka ƙara shuka amfanin gona masu tsawo ba domin suna iya ɓoye ’yan ta’adda.

Saboda haka kana shuka wake da gyada kawai, amma amfanin da kake samu ba ya taɓa isa. Kuma duk lokacin da ka taka gona, ka san akwai yiwuwar ka ji karar harbe-harbe, sai ka tsere don ceton ranka.

A wannan shirin na #BirbishinRikici, mun ba da labarin Hannatu Isiah, wata manomiya a Madagali, wata ƙaramar al’umma a Jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya, wadda ta kasa ciyar da kanta ko samun kuɗin amfani sakamakon rashin tsaro.


Mai Gabatarwa: Rukayya Saeed

Marubuciya: Sabiqah Bello

Muryoyin Shiri: Hajara Ibrahim

Fassara: Rukayya Saeed

Edita: Aliyu Dahiru

Furodusa: Al-amin Umar

Babban Furodusa: Anthony Asemota

Babban Mashiryi: Ahmad Salkida

Source link

Leave a Reply

Discover more from Occasional Digest

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading